Svoboda | Graniru | BBC Russia | Golosameriki | Facebook

Accessibility links

Labari da Dumi-Duminsa

Cisse-Ya Biyo Sawun CAF Wurin Maida Martani Ga De Laurentiis Kan Sukar 'Yan Wasan Afrika


African Footballer of the Year Awards
African Footballer of the Year Awards

Kocin Senegal Aliou Cisse ya ce wasan kwallon kafa na kasa-da-kasa - da kuma musamman gasar cin kofin kasashen Afirka – ba zai yiwu ya wasa mai martaba na biyu ba ga wasanni kulob kulob a Turai, ya kuma kalubalanci Napoli da ta ce kada a kara sayin ‘yan wasan Afirka.

Kalaman na dan shekaru 46 da haifuwan na zuwa ne bayan da shugaban kungiyar Napoli Aurelio de Laurentiis ya ce kungiyar ta kasar Italiya zata daina daukar ‘yan wasa daga Afrika, har sai sun amince da ba zasu yi wasa a gasar cin kofin Afrika da ake yi a duk shekaru biyu ba.

Cisse ya fadawa shirin BBC Sports Africa cewa, dan wasa zai iya yin wasa cikin kungiyoyi 12, amma kungiyar wasa ta kasa kwaya daya kacal.

'Yan wasa Ghana suna atisaye a birnin Doha (Facebook/Hukumar kwallon kafar Ghana)
'Yan wasa Ghana suna atisaye a birnin Doha (Facebook/Hukumar kwallon kafar Ghana)

“Kulob kulob ba za su taba kasancewa sama da tutarmu da kungiyar kasarmu ba. Kuma duk dan Senegal da ke taka leda a Turai, a duk inda yake, idan ya cancanta zan kira shi don ya kare tutar kasar.

"Ina matukar girmama (De Laurentiis) amma ina kalubalantarsa a kan kokarin hana daukar 'yan wasan Afirka."

Magoya bayan kungiyar kwallon kafa ta Najeriya "Super Eagles" a filin wasa na kasa dake Abuja, inda aka lallasa 'yan Ethiopia da ci 4 da babu, lahadi 27 Maris, 2011
Magoya bayan kungiyar kwallon kafa ta Najeriya "Super Eagles" a filin wasa na kasa dake Abuja, inda aka lallasa 'yan Ethiopia da ci 4 da babu, lahadi 27 Maris, 2011

Lokacin da ake gudanar da gasar cin kofin Afrika - wanda aka saba yi a watan Janairu da Fabrairu shekaru biyu - yana haifar da rashin fahimta tsakanin ‘yan wasa da kungiyoyin Turai na tilasta musu sakin 'yan wasa a tsakiyar kakar wasa.

Napoli ta yi rashin dan wasan baya Kalidou Koulibaly - wanda ya jagoranci Senegal ta samu nasarar lashe gasar cin kofin kasashen Afirka ta 2021 da aka shirya a bana a Kamaru - da kuma dan wasan tsakiya Andre-Frank Zambo Anguissa don yiwa kasarsa wasa a gasar, yayin da tsaka da kakar bara sannan su biyun ba su buga wasanni shida ba a kungiyar.

Kofin Duniya ta Qatar 2022

Kofin Duniya ta Qatar 2022
please wait

No media source currently available

0:00 0:00:32 0:00
Karin bayani akan Kofin Duniya ta Qatar 2022

Ronaldo vs. Messi

Ronaldo vs. Messi
please wait
Embed

No media source currently available

0:00 0:01:24 0:00
Satumba 30, 2020

Ronaldo vs. Messi

Karin bayani akan Wasanni
XS
SM
MD
LG