Wasu jerin hare-hare da jiragen yakin Isra'ila suka kai kudancin Lebanon sun kashe mutane 16, yayin da wasu rokoki da kungiyar Hezbollah ta harba ta yi sanadiyyar mutuwar wani Ba'isra'ile daya, wanda ya zamar da ranar Laraba nan mafi muni cikin sama da watanni biyar na gwabza fada a kan iyakar kasar