Sheinbaum, masaniyar kimiyyar yanayi kuma tsohuwar shugaban birnin Mexico, ta lashe zaben shugaban kasa da kashi 58.3% zuwa 60.7% na kuri'un da aka kada, bisa ga kididdigar da hukumar zabe ta Mexico ta fitar.
Jam’iyyar wadda Nelson Mandela ya taba jagoranta ta lashe kujeru 159 ne kacal a cikin 400 inda a baya ta samu kujeru 230.
Daruruwan mutane ne suka gudanar da faretin bikin ranar Isra'ila a birnin New York a ranar Lahadin da ta gabata, inda suka yi kira da a sako mutanen da kungiyar Hamas ta yi garkuwa da su a Gaza.
Akalla mayaka masu goyon bayan gwamnatin kasar Iran 12 ne aka kashe a wani harin da Isra’ila ta kai cikin dare kan wata masana’anta da ke kusa da Aleppo a arewacin Syria, kamar yadda wata kungiya mai zaman kanta ta sanar a safiyar yau Litinin.
Wasu mazauna Kaduna a Najeriya sun bayyana matakin da su ke dauka don ganin suna shaker iska mai kyau
Wata kwararriya a Maiduguri, Dr Aida Abba Wajes ta yi karin haske akan illolin gurbatacciyar iska ga lafiyar mutane da kuma matakan da za a iya dauka.
An samu sarakuna biyu da kowannensu ke zaman fada a matsayin sarkin Kano a lokaci guda. Yayin da Muhammadu Sanusi da gwamnatin jihar ta mayar da ya rika karbar gaisuwa da mubaya’a a babban gidan sarautar, shi kuwa Aminu Ado Bayero, ya rika yin na shi zaman fada ne a gidan sarki dake Nasarawa GRA.
A kasar Kenya, daliban wata makaranta dake kusa da inda ake zubar da shara mafi girma a kasar sun fara dashen itatuwan gora don bunkasa ingancin iska a yankin.
Ingancin iskar da muke shaka kullum yana da tasiri ga lafiyar mu. Sinadarin Sulfor dioxide da sinadarin carbon monoxide suna daga cikin sinadaren da suke gurbata iskar da muke shakka a fadin duniya.
Dambarwar sarauta a masarautar Kano ta sa a karon farko cikin tarihi, an samu sarakuna biyu da kowanne ke zaman fada a matsayin sarkin Kano – kuma a cikin birin na Kano
Farfesa Tijjani Naniya wani masanin tarihi a jami’ar Bayero dake Kano ya yi bayani kan inda dambarwar Kano ta samo asali.
Ana sa ran fitar da cikakken sakamakon zaben a karshen makon nan da mu ke bankwana da shi.
Falasdinawa a birnin Rafah da ke kan iyaka sun ba da rahoton kazamin fada a 'yan kwanakin nan, yayin da sojojin Isra'ila ke kara fadada hare-haren da suke kai wa a kudancin kasar, tare da kwace iko da daukacin iyakar Gaza da Masar.
Rundunar sojin Najeriya ta bayyana a ranar Juma’a cewa ‘yan aware a yankin kudu maso gabas sun kashe sojoji biyar a wani hari da suka kai a wani shingen binciken ababan hawa.
Mazauna Rafah sun ba da rahoton mummunar luguden wuta da harbin bindiga a yau Alhamis a birnin Gaza mai nisa da ke kudu bayan da Isra'ila ta ce ta kwace wata hanya mai mahimmanci a kan iyakar Falasdinawa da Masar.
A ranar Alhamis ne za a kashe wani mutum mai shekaru 50 da haihuwa ta hanyar yin allura mai guba a jihar Alabama da ke Kudancin Amurka bisa laifin kashe wasu tsofaffin ma'aurata.
Domin Kari