Svoboda | Graniru | BBC Russia | Golosameriki | Facebook

Accessibility links

Labari da Dumi-Duminsa

Gasar AFCON: “Kun Nuna Jajircewa Matuka”, Tinubu Ya Jinjinawa Tawagar Super Eagles


Shugaban Kasar Najeriya, Bola Ahmed Tinubu
Shugaban Kasar Najeriya, Bola Ahmed Tinubu

Shugaban kasa Bola Tinubu ya yabawa irin kwazon da Tawagar Super Eagles ta nuna a wasan karshe na gasar cin kofin nahiyar afrika (AFCON) data gudana a kasar Ivory Coast.

Duk da rashin nasarar da suka yi a hannun masu masaukin baki, Tinubu yace Super Eagles ta nuna kwarewa da jajircewa a gasar.

Hakan na kunshe ne a cikin sanarwar da hadimin shugaban kasar akan harkokin yada labarai, Ajuri Ngelale, ya fitar a lahadin data gabata.

Ivory Coast ce tayi nasara a wasan karshe na gasar afcon ta 2023 bayan data doke takwararta ta super eagles da ci 2 da 1.

Tinubu ya kara da cewar tawagar Najeriyar ta samu gagarumar nasara a idanun al’ummar nahiyar Afrika dama duniya baki daya.

A cewar sanarwar, Shugaba Bola Tinubu ya yabawa tawagar Super Eagles saboda irin kwazon da suka nuna a wasan karshe na gasar cin kofin nahiyar Afrika data gudana a kasar Ivory Coast.

Dandalin Mu Tattauna

Kofin Duniya ta Qatar 2022

Kofin Duniya ta Qatar 2022
please wait

No media source currently available

0:00 0:00:32 0:00
Karin bayani akan Kofin Duniya ta Qatar 2022

Ronaldo vs. Messi

Ronaldo vs. Messi
please wait
Embed

No media source currently available

0:00 0:01:24 0:00
Satumba 30, 2020

Ronaldo vs. Messi

Karin bayani akan Wasanni
XS
SM
MD
LG