Svoboda | Graniru | BBC Russia | Golosameriki | Facebook

Accessibility links

Labari da Dumi-Duminsa

'Yan Bindiga Sun Sake Sakin Wasu Fasinjojin Jirgin Kasa Guda Bakwai Da Aka Yi Garkuwa Da Su


'Yan Bindiga Sun Sake Sakin Wasu Fasinjojin Jirgin Kasa Guda Bakwai Da Aka Yi Garkuwa Da Su
'Yan Bindiga Sun Sake Sakin Wasu Fasinjojin Jirgin Kasa Guda Bakwai Da Aka Yi Garkuwa Da Su

Bayan kwashe sama da kwanaki 135, 'yan-bindigan da su ka sace mutane a jirgin kasan Abuja-Kaduna sun sake sako wasu mutane bakwai a yau Laraba sakamakon shiga tsakani da daya daga cikin malaman addinin Musulunchi, Dr. Ahmad Mahmud Gumi ya yi.

WASHINGTON, D.C - Jinkirin sakin sama da mutane 60 da 'yan-bindiga su ka sace a jirgin kasan Abuja-Kaduna dai ya sa dole 'yan'uwan wadanda aka sacen kai-komon ganin 'yan'uwan su su kubuta abun da ya sa 'yan-bindigan ke ta sakin fasinjojin jirgin kasan kashi-kashi kuma wadanda aka sako yau Laraba duka 'yan gida daya, banda wata dattijuwa 'yar shekara 60 da aka ce ciwo ne ya yi tsanani aka saka ta cikin wadanda aka sako.

'Yan Bindiga Sun Sake Sakin Wasu Fasinjojin Jirgin Kasa Guda Bakwai Da Aka Yi Garkuwa Da Su
'Yan Bindiga Sun Sake Sakin Wasu Fasinjojin Jirgin Kasa Guda Bakwai Da Aka Yi Garkuwa Da Su

Shugaban kamfanin jaridar Desert Herald, Malam Tukur Mamu ya ce a ma daina boye-boye akan amfani da kudi wajen ceto wadanda ke dajin.

Malam Abubakar Idris Garba mai-dakin matar da aka sako kuma mahaifin yaranta da aka sako a wannan Laraba ya ce ya na da roko ga gwamnatin tarayya.

'Yan Bindiga Sun Sake Sakin Wasu Fasinjojin Jirgin Kasa Guda Bakwai Da Aka Yi Garkuwa Da Su
'Yan Bindiga Sun Sake Sakin Wasu Fasinjojin Jirgin Kasa Guda Bakwai Da Aka Yi Garkuwa Da Su
'Yan Bindiga Sun Sake Sakin Wasu Fasinjojin Jirgin Kasa Guda Bakwai Da Aka Yi Garkuwa Da Su
'Yan Bindiga Sun Sake Sakin Wasu Fasinjojin Jirgin Kasa Guda Bakwai Da Aka Yi Garkuwa Da Su

Har yanzu dai fasinjojin jirgin kasan 27 na daji kuma mahafiya da ya’yan Abdul-Azeez Attah na cikin wadanda ba a sako ba saboda haka ya ce su na cikin damuwa.

Wasu 'yan'uwan da ba a sako na su ‘yanuwan ba sun shedawa Muryar Amurka cewa kudi ake bukata wanda ba su da shi amma su nan su na ta karo-karo.

Saurari cikakken rahoton daga Isah Lawal Ikara:

'Yan Bindiga Sun Sake Sakin Wasu Fasinjojin Jirgin Kasa Guda Bakwai Da Aka Yi Garkuwa Da Su.mp3
please wait

No media source currently available

0:00 0:04:02 0:00

XS
SM
MD
LG